in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya rattaba hannu kan kasafin kudin kasar na 2016
2016-05-07 11:56:21 cri
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi wa kasafin kudin kasar na shekarar 2016 taken kasafin kudi don kawo sauyi, sannan ya ambata cewa kasafin kudin kasar zai bada gwamnatinsa damar cika alkawurran da ta daukawa jama'ar kasar.

A jiya Juma'a ne dai shugaban na Najeriya ya rattaba hannu kan kasafin kudin kasar na bana wanda adadinsa ya kai naira triliyan 6 da biliyan 600 kwatankwacin dalar Amurka biliyan 30 da miliyan 400, bisa kiyasin gangar danyen mai kan dala 38 a kan kowace ganga.

Sannann an tsara kasafin kudin ne bisa hasashen samar da ganga miliyan 2 da dubu 200 na danyan man a kowace rana a kasar.

Bikin sanyan hannu kan kasafin kudin ya samu halartar mataimakin shugaban kasar Yemi Osinbajo, da shugaban majalisar dattijai Bukola Saraki, da na wakilai Yakubu Dogara da shugaban jam'iyyar APC mai mulki John Odigie-Oyegun.

A yayin jawabinsa, shugaba Buhari ya nuna farin cikinsa game da sanya hannu kan kasafin kudin kasar, sannan ya yabawa bangaren majalisun dokokin kasar bisa hadin kan da suke baiwa bangaren zartaswa.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China