in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya za ta bunkasa harkokin gwamnati ta hanyar amfani da dokar samar da bayanai
2016-05-05 09:37:49 cri
Gwamnatin Najeriya ta jaddada aniyarta na samar da gwamnati mai tsabta ta hanyar aiwatar da dokar 'yancin tattara bayanai wato FOI a takaice.

Ministan yada labarai da raya al'adu na kasar Lai Muhammad ne ya bayyana aniyar gwamnatin a sakonsa na bikin ranar 'yan jarida ta duniya, wanda aka gudanar a ranar Talatar da ta gabata a Abuja fadar mulkin kasar.

Minsitan ya ce dokar ta FOI za ta kasance a matsayin wani muhimmin makami da za'a yi amfani da shi wajen yaki da rashawa da kuma samar da budaddiyar gwamnati a kasar.

Lai Muhammad ya ce, gwamnati ta dauki wasu kwararan matakai bama ga tabbatar da 'yancin fadin albarkacin baki ba, har ma da ba da damar samun muhimman bayanai. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China