in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kakakin majalissar dokokin Cote d'Ivoire ya yi kira da a kara azama game da yaki da ta'addanci
2016-05-06 19:32:53 cri
Kakakin majalissar dokokin kasar Cote d'Ivoire Guillaume Soro, yayi kira da a dauki karin matakai da suka dace, game da yaki da ayyukan ta'addanci.

Mr. Soro, wanda ya yi wannan kira a birnin Abidjan, yayin taron 'yan majalissun dokokin Afirka da na kasashen larabawa, ya ce akwai bukatar hadin gwiwa da goyon bayan juna, tare da kara jan hankalin dukkanin masu ruwa da tsaki, wajen tabbatar da nasarar wannan buri.

Ya ce musayar bayanai da kwarewa, da kuma samar da isassun kayan aikin da ake bukata, na sahun gaba wajen tabbatar da nasarar yaki da ayyukan ta'addanci.

Dandalin 'yan majalissun kasashen Afirka da na kasashen Larabawa na da nufin hada bangarorin 'yan majalissun sassan biyu, domin tattauna batutuwa da suka jibanci yankunan su cikin hadin gwiwa.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China