in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD za ta rage yawan jami'anta a Cote d'Ivoir
2016-01-21 10:06:38 cri
A ranar Larabar nan ne, kwamitin tsaro na MDD ya zartar da wani kuduri na zaftare adadin jami'an soji da ya tura aikin wanzar da zaman lafiya a Cote d'Ivoire wato (UNOCI) daga adadin dakaru 5,437 zuwa 4,000 kuma wannan tsari zai fara aiki ne daga ranar 31 ga watan Maris na wannan shekara.

A yayin da take kokarin amincewa da wannan shiri, MDD ta bayyana halin da ake ciki a kasar Cote d'Ivoire da cewar lamari ne dake barazana ga sha'anin tsaro a fadin yankin bakin daya.

To sai dai kwamitin MDD ya gamsu cewar, zaben shugaban kasar da aka gudanar cikin nasara a ranar 25 ga watan Octoban shekarar 2015, tamkar aza wani harsashen gina dawwamamman zaman lafiya ne a kasar Cote d'Ivoire wacce ta jima tana fuskantar tashe-tashen hankula.

Bugu da kari, kwamitin mai mambobi 15, ya yi na'am da ci gaban shirin wanzar da zaman lafiya na kasar, domin tabbatar da samun daidaito, da kwanciyar hankali, da tsaro da adalci da kuma farfado da cigaban tattalin arziki a kasar.

MDD ta yanke shawarar rage adadin jami'an aikin wanzar da zaman lafiyar ne bisa la'akari da rahoton da aka gabatarwar ofishin babban sakataren MDD a ranar 8 ga watan Disambar shekarar 2015.

An kafa tawagar UNOCI ne a shekarar 2004, domin samar da zaman lafiya da hada kan bangarorin da ba sa ga maciji da juna a kasar wanda aka rattaba hannu kansa tun a shekarar 2003. Sai dai a sakamakon barkewar wani sabon rikici bayan zaben shugaban kasar a shekarar 2010, UNOCI, ta ci gaba da aiki a kasar, domin kare fararen hular kasar da tallafawa gwamnatin kasar wajen fatattan 'yan tada kayar baya domin maido da zaman lafiya da kuma mutunta yancin bil adama a kasar. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China