in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi Allah wadai da harin kasar Cote d'Ivoire
2016-03-15 10:27:35 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya fidda sanarwa a jiya Litinin, inda ya yi Allah wadai da hare-haren da dakarun suka kai a wasu otel dake garin Grand Bassam dake kudu masu gabashin kasar Cote d'Ivoire a ranar Lahadin da ta gabata.

Cikin sanarwar, kwamitin sulhu na MDD ya mika ta'aziya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu sakamakon harin, sanna ya nuna juyayi ga gwamnatocin kasashen Cote d'Ivoire, Faransa da dai sauran gwamnatocin kasashe na wadanda suka rasu sakamakon hare-haren.

Kaza lika, ya ce, kwamitin yana goyon bayan kasar Cote d'Ivoire da sauran kasashen dake yaki da ta'addanci, sa'an nan ya jaddada cewa, ya kamata a karfafa ayyukan kasa da kasa da na shiyya-shiyya domin yaki da kungiyoyin 'yan ta'adda da masu tsattsauran ra'ayi. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China