in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A kalla mutane 19 sun hallaka sanadiyar harin kunar bakin wake sau biyu a Kamaru
2016-02-19 20:15:24 cri
Rahotannin daga Younde, babban birnin kasar Kamaru ya tabbatar da cewar harin kunar bakin wake har sau biyu da suka abku a Jumm'an nan a wani kasuwa a jihar arewa mai nisa dake kan iyaka da Nigeriya ya yi sanadiyar mutuwar mutane 19, sannan wadansu guda 50 suka jikkata.

Kamar yadda majiyar tsaro ta tabbatar wadansu matasa ne su biyu dauke da ababen fashewar suka dana shi bayan da suka nade jikin su a cikin kasuwan, wanda nan take ya hallaka mutane 10 yayin da wasu suka hallaka.

Bayan kai wadanda suka jikkata asibiti wasu daga cikin su daga baya sun mutu adadin da ya sa matattun ya kai 19, ciki har da matasan da suka kai harin su biyu.

Babu wani kungiyar ko mutumin da ya dauki nauyin harin, amma ma'aikatan leken asiri na kasar Kamaru sun tabbatar da cewar suna nuna yatsa ga kungiyar Boko Haram, kungiyar ta'addanci a Nigeriya da suke ta kai hari a jihar dake yankin arewa mai nisa. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China