in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka rasu a sakamakon harin bom da aka kai a kudancin Iraki ya karu zuwa 32
2016-05-02 12:22:38 cri
Wata fashewar tagwayen boma-bomai da ta auku a kudancin kasar Iraki a ranar Asabar, ta haddasa rasuwar mutane a kalla 32, tare da raunata wasu mutanen 75.

Wasu motoci biyu bakare da boma-bomai ne suka tarwatse a dab da wani ginin gwamnati dake birnin Samawah na jihar Liwa' Al muthanna, da kuma wani wurin ajiye motoci dake cibiyar birnin.

Rahotanni daga majiyar 'yan sandan wurin sun ce mai yiwuwa ne yawan mutanen da suka mutu a sakamakon tashin bama-baman zai ci gaba da karuwa.

Tuni dai kungiyar IS ta sanar da daukar alhakin wannan hari, kungiyar da a baya ta sha kai makamantan wadannan hare hare a wurare daban daban na kasar Iraki.

Yanzu haka dai, kungiyar tana rike da ikon yawancin yammaci da arewacin kasar Iraki, kana suna musayar wuta tare da sojojin gwamnatin kasar a jihohi da dama.

Sojojin gwamnatin Iraki sun sanar da daukar matakan soji domin kwace ikon birnin Mosul cikin watan Maris, kafin daga bisani mayakan kungiyar ta IS su maida martani da manyan hare-hare. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China