in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Adadin mutanen da suka mutu a harin bam din Iraki ya karu zuwa 53
2016-02-29 20:40:02 cri
Rahotanni daga kasar Iraki na bayyana cewa, yawan mutanen da suka bakunci lahira a harin tagwayen bama-baman da aka kai jiya Lahadi a wata kasuwa mai cike da jama'a a birnin Bagadaza na kasar Iraki yanzu haka ya tasamma 53.

Alkaluman baya-bayan da ma'aikatar harkokin cikin gidan kasar Iraki ta fitar ya nuna cewa, baya ga wannan adadi akwai kuma mutane 117 da suka jikkata daga harin da aka kai kasuwar Mreidy da ke gundumar Sadar.

Maharan dai sun yi amfani da tsohon salo na kai hari ne, inda suka tayar da bam na farko domin su janyo hankalun jami'an tsaro da sauran jama'a, kafin daga bisani su tayar da bam na biyu, wanda ya yi mummunan barna.

Sa'o'i bayan tayar da wadannan bama-bamai ne, sai kungiyar IS ta sanar da daukar alhakin kaddamar da hare-hare. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China