in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tagwayen boma bomai sun hallaka mutane 23 da raunata wasu 59 a Bagadaza
2016-02-29 10:35:53 cri
A kalla ma mutane 23 ne aka tabbatar da mutuwarsu, sannan wasu 59 suka samu raunuka a yayin fashewar wasu tagwayen boma bomai a gabashin Bagadaza na kasar Iraqi.

Wata majiya daga ofishin ministan harkokin cikin gidan kasar ta shedawa kamfanin dillanin labaran kasar Sin Xinhua cewar, harin an kaddamar da shi ne a kasuwar Mreidy dake unguwar Sadr.

Majiyar ta kara da cewar, yan kunar bakin wake sun tada bomai bomai da ke jikinsu ne a kasuwar wacce ke da cunkoson jama'a kuma galibin jama'ar dake taruwa mabiya shi'a ne.

Fashewar tayi sanadiyyar lalata shaguna da dama dake kusa da inda abin ya faru, kuma motoci da dama sun kama da wuta.

Maharan dai sun yi amfani ne da wani salo, inda suka tada bam na farko don a samu taruwar jami'an tsaro da sauran jama'a, yayin da suka tada bam na biyu wanda ya haddasa mummunar barna.

A halin yanzu, Iraqi na fuskantar tashe tashen hankula, tun bayan da kungiyar IS mai da'awar kafa daular Islama ta kame wasu yankuna da dama a arewaci da yammacin kasar a watan Yunin shekarar 2014.

Tun da farko rahoton MDD ya nuna cewar, sama da mutane dubu 22,300 ne aka kashe a Iraqi a shekarar 2015.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China