in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun yan adawa a Sudan ta Kudu sun koma babban birnin kasar
2016-04-11 20:39:33 cri
Rukuni na karshe na dakarun madugun 'yan adawa a Sudan ta Kudu kuma tsohon mataimakin shugaban kasar Riek Machar, ya koma birnin Juba a ranar 10 ga wata, bayan cika sharrudan da mista Machar ya gabatar, don kafa gwamnatin wucin gadi ta hadin gwiwa a kasar.

A watan Febrairu na bana, shugaban kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir ya bayar da sanarwa, inda ya yi kira ga Machar da ya koma birnin Juba cikin hanzari, don shiga shirin kafa gwamnatin wucin gadi a kasar don cimma yarjejeniyar warware rikicin kasar Sudan ta Kudun tsakanin bangarorin biyu kamar yadda suka daddale a shekarar bara.

Machar ya bayyana a kwanakin baya cewa, idan dakarunsa sun koma birnin Juba, zai tashi zuwa birnin Juba don shiga shirin kafa gwamnatin wucin gadi a ranar 18 ga wannan wata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China