in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Akinwunmi Ambode ya nuna yabo kan ziyarar shugaba Buhari a kasar Sin
2016-05-01 13:00:44 cri
Ofishin karamin jakadan kasar Sin a birnin Ikkon kasar Najeriya ya ba da labarin kan shafin yanar gizonsa cewa, gwamnan jihar Legas Akinwunmi Ambode ya gana da shugaban kasar Tarayyar Najeriya Muhammadu Buhari a ranar 30 ga watan Afrilu, inda a bayan ganawarsu, gwamna Ambode ya bayyana wa manema labaru cewa, ziyarar da shugaba Buhari ya yi a kasashen waje ta janyo ma kasar karin jarin waje da take bukata.

Gwamnan ya kara da cewa, ziyarar da shugaban ya yi a kasar Sin, ta sa bangarorin 2 sun kulla yarjeniyoyi daban daban da suka shafi aikin samar da wutar lantarki, da hakar ma'adinai, da zirga-zirgar motoci, da aikin gona, da dai makamantansu. A cewar gwamnan, hakan zai ciyar da tattalin arzikin kasar gaba, gami da amfana wa daukacin al'ummar kasar.

A bangaren jihar Legas kuwa, in ji gwamnan, ta samu moriya sosai bisa manyan ayyukan da aka kulla tsakanin Najeriya da Sin, wadanda suka hada da gina layin dogo na karamin jirgin kasa wanda zai shafe dalar Amurka biliyan 2.5, gami da babban layin dogon da zai hada jihar Legas da ta Kano.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China