in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta bude kofar zuba jari daga kasar Sin
2016-04-26 09:29:33 cri
Ministan ma'aikatar masana'antu, cinikayya da zuba jari na tarayyar Najeriya Okechukwu Enelamah, ya ce Najeriya na da kudurin aiwatar da manufofin zuba jari na tsawon lokaci tsakaninta da kasar Sin. Mr. Enelamah ya ce hakan na kunshe cikin albishir da shugaban Najeriya ya zo wa al'ummar kasar da shi daga ziyarar da ya gudanar a kasar Sin.

Ministan wanda ya bayyana hakan jiya a birnin Ikkon jihar Lagos, ya yi fatan ci gaba da zurfafa huldar cinikayya tsakanin sassan biyu. A cewar sa cimma nasarar fadada alakar Najeriya da Sin ta fuskar cinikayya, zai taimakawa sassan biyu wajen cin gajiya tare, da ma nahiyoyin da suke ciki.

Mr. Enelamah ya kara da cewa Najeriya na iya koyin hadin gwiwa da kasar Sin ta fuskokin tsarin gudanarwa, da yadda Sin ta fidda dunbin al'ummunta daga fatara cikin 'yan shekaru kalilan.

Daga nan sai ya bayyana burin gwamnatin kasar mai ci na zamanintar da masana'antu, da samar da kyakkyawan yanayin kasuwanci, da hada hadar cinikayya yadda ya kamata. Kaza lika a cewarsa Najeriya na da burin rage gibin cinikayya, wanda hakan zai taimaka wajen bude kofar zuba jari, wadda tuni kasar Sin ta bayyana goyon bayan ta ga wannan mataki. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China