in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya zata fadada sintiri a tekun Guinea
2016-04-29 09:47:03 cri
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya fada cewa hadaddiyar rundunar tabbatar da tsaro zata fara aikin sintiri ta ruwa zuwa tekun Guinea.

Buhari, ya bayyana hakan ne a jiya Alhamis, a loakcin tattaunawa da ministan tsaron kasar Faransa Jean-Yves Le Drian, a Abuja fadar mulkin kasar.

Ya ce kasarsa za ta cigaba da tsaurara matakan tsaro a yankin, domin samar da ingantaccen tsaro, da kuma dakile aniyar masu satar danyen mai da masu fashin jirgin ruwa.

Da ma dai akwai dakarun tsaro na kawance daga kasashen Najeriyar, da Chadi, da Kamaru, da Nijer da kuma jamuhuiriyar Benin, wadanda ke yaki da mayakan Boko Haram a shiyyar arewa maso gabashin Najeriyar.

Ya ce a halin yanzu dakarun Najeriyar suna cigaba da yin lugudan wuta kan mayakan a dajin Sambisa.

Shugaba Buhari, ya lashi takobin murkushe mayakan na Boko Haram, wadanda suka hallaka mutane sama da 10,000, tun bayan kaddamar da hare hare a shekarar 2009. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China