in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
HCR:'Yan kasar Burundi na cigaba da ficewa daga kasarsu
2016-04-23 12:38:45 cri
Bayan shekara daya a farkon barkewar rikicin kasar Burundi, kusan mutane dubu 260 suka fice daga kasarsu zuwa kasashe makwabta a yayin da kuma wasu duban mutane za su iya zuwa su iske sauran nan da karshen shekara, idan ba a samu wata mafitar siyasa ba domin kaucewa wani yakin basasa, in ji babbar hukumar 'yan gudun hijira ta MDD (HCR).

Mutane na ci gaba da shiga kasashe makwabta, amma cikin karamin adadi a 'yan makwannin baya bayan nan, a yayin da abubuwa suke matukar wahala na ratsa kan iyakoki. Mutane da dama dake neman hijira da sabbin zuwa na bayyana cin zarafin dan Adam da ake ci gaba da yi a kasar Burundi, da suka hada azabtarwa, fyade, tsare mutane ba bisa doka ba, takurawa, tilastawa mutane shiga kungiyoyin sa kai, kisan kai da makamantan haka, in ji kakakin HCR, a cikin sanarwar MDD.

A cewar HCR, ci gaban tallafin kasa da kasa na da muhimmanci sosai wajen rage zaman dar dar da kuma taimakawa yin shawarwarin tsakanin bangarori masu gaba da juna na kasar ta Burundi. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China