in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyya mai mulki a Burundi ta nemi a tattauna game da zaben kasar a 2020
2016-04-27 09:51:15 cri
Jam'iyya mai mulkin kasar Burundi ta ba da shawarar a shiga tattaunawa domin shirye shiryen tunkarar zaben kasar a shekarar 2020 da nufin kawo karshen rikicin siyasar da ya dabaibaye kasar.

Shugaban jam'iyyar mai mulkin kasar Pascal Nyabenda ya furta hakan ne a ranar cika shekara guda da bayyana shugaban kasar mai ci Pierre Nkurunziza a matsayin dan takarar zabe na jam'iyyar don neman wa'adin mulki karo na 3, lamarin da ya haifar da rikici da zanga zanga a fadin kasar.

Nyabenda ya fada cewa tattaunawar za ta duba yadda jam'iyyun siyasar kasar za su gyara kura kuran da aka tafka a lokacin zaben shekarar 2015.

Shugaba Nkurunziza yayi nasarar lashe zaben kasar a watan Yulin shekarar bara, bayan dakile wani yunkurin juyin mulki da bai samu nasara ba.

Sai dai 'yan adawa a kasar na zargin cewa, sake zaben nasa ya ci karo da dokokin kundin tsarin mulkin kasar, wanda ya sahhale wa'adin mulki biyu na shugaban kasar kacal.

Sama da mutane 400 ne aka hallaka a lokacin zanga zanga a kasar ciki har da wasu manyan hafsoshin sojan kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China