in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadan Sin ya ce tattaunawar siyasa ce za ta magance rikicin Burundi
2016-04-02 17:52:29 cri
Gwamnatin kasar Sin ta bayyana cewar, rikicin kasar Burundi za'a iya kawo karshen sa ne ta hanyar tattaunawar siyasa.

Zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Liu Jieyi, ya bayyana hakan a Juma'ar da ta gabata.

Mista Liu ya ce, burin kasar Sin game da wannan batu shi ne, tana karfafa gwiwa ga kasashen nahiyar Afrika da su tashi tsaye wajen gayyato dukkanin bangarorin da ba sa ga maciji da juna, don zama a teburin sulhu domin warware rikicin kasar.

Ya kara da cewa, kasar Sin ta bayyana matsayinta game da rikicin Burundin da cewar, tattaunawar sulhu ce kadai za ta kawo karshen dambarwar siyasar kasar ta Burundi, kuma wannan kudurin ya samu amincewar wakilai 15 na kwamnitin MDD.

MDD ta nemi kasashen dake yankin da su bada gudumawa don warware rikicin siyasar da yaki ci yaki cinyewa a kasar Burundin, kuma a dauki dukkan matakan dakile ayyukan 'yan tawaye masu dauke da makamai. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China