in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Chadi: Shugaba Deby ya sake lashe da kashi 61 cikin 100 na kuri'un da aka kada
2016-04-22 10:15:43 cri
An sake zaben shugaban kasar Chadi Idriss Deby Itno, tun a zagayen farko na zaben shugaban kasa na ranar 10 ga watan Afrilu na shekarar 2016 da kashi 61.56 cikin 100 na kuri'un da aka jefa, gaban 'yan takara goma sha biyu, a cewar sakamakon wucin gadi da hukumar zabe mai zaman kanta (CENI) ta gabatar a ranar Alhamis. Shugaban 'yan adawa wanda ya zo na biyu, Saleh Kebzabo ya samu kashi 12.80 cikin 100 na kuri'un da ka jefa, yayin da Laoukein Kourayo Medard, magajin garin hedkwatar tattalin arziki, Moundou ya zo na uku da kashi 10.69 cikin 100 da kuri'in da aka kada.

Tsohun faraminista, Joseph Djimrangar Dadnadji, wanda ya koma adawa ya samu kashi 5 cikin 100 na kuri'un da aka jefa.

A ranar 10 ga watan Afrilu, kashi 76.11 cikin 100, kimanin miliyan 6.2 na 'yan Chadi da suka yi rijistan zabe sun fito domin zaben sabon shugaban kasa. A ranar Laraba, 'yan takara takwas sun yi barazanar kafa wata "gwamnatin ceton kasa" idan har hukumar zabe ta sanar da shugaba mai ci a matsayin wanda ya lashe zabe.

Haka kuma sun yi kashedi ga hukumar zabe da kwamitin tsarin mulki kan duk wani yunkurin tabbatar da wannan satar zabe, tare da niyyarsu ta kin amincewa da hukumomin da za su biyo bayan wannan satar zabe, idan ba su samu biyan bukatunsu ba za su kafa wata gwamnatin ceton kasa domin amsa bukatun 'yan kasar Chadi, in ji sanarwar wadannan 'yan takara takwas. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China