in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi kira ga kasa da kasa da su hada kai wajen yaki da ta'addanci
2016-03-25 10:03:47 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon, ya yi kira ga kasashen duniya da su hada kai da juna, wajen yaki da ta'addanci da tsattsauran ra'ayi.

Ban Ki-moon ya bayyana hakan ne a gun taron manema labaru da aka gudanar, bayan kammala shawarwari da firaminsitan kasar Lebanon Tammam Salam a birnin Beirut.

Mr. Ban ya ce kamata ya yi kasashen duniya su kara kokari wajen yaki da ta'addanci. Ya ce ya kamata sassan kasa da kasa su sa ido, tare da hada kai wajen tinkarar tsattsauran ra'ayin addini da 'yan ta'adda.

Kaza lika ya bayyana kawar da tushen ta'addanci, da na tsattsauran ra'ayi, a matsayin aikin mafi muhimmanci da ya dace a ci gaba da aiwatarwa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China