Shugaban jamhuriyar Nijer Mahamadou Issoufou ya sanya hannu kan umurnin shugaba a jiya Litinin, domin kafa sabuwar gwamnatin.
Sabuwar gwamnatin kasar ta hada da jami'ai 38, ciki har da ministoci mata 5. Sa'an nan, ministoci 5 na tsohuwar gwamnati da suka hada da na ma'adinai da makamashi da kasuwanci da inganta bunkasuwar kamfannoni masu zaman kansu sun ci gaba da rike da mukamansu.
A ranar 2 ga wannan wata, Mahamadou Issoufou wanda ya lashe zabe ya yi rantsuwar kama aiki, don fara wa'adinsa na biyu a matsayin shugaban kasar ta Nijer.(Lami)