in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya taya Muhammadu Buhari murnar cin zaben kasar Nijeriya
2015-04-02 10:22:27 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya bayar da sanarwa ta kakakinsa a ranar laraba 1 ga wata, inda ya taya Muhammadu Buhari murnar cin zaben shugaban kasar Nijeriya.

Sanarwar ta bayyana cewa, a ganin Ban Ki-moon, yadda aka cimma nasara a kokarin gudanar da zaben shugaban kasar Nijeriya ya shaida cewa, ana bin tsarin demokradiyya a kasar, kuma yana fatan za a ci gaba da bin wannan tunanin a zaben gwamnonin jihohin da na 'yan majalisar dokokin kasar da za a gudanar a ranar 11 ga wata.

sanarwar har ila yau ta ce, Ban Ki-moon ya yaba ma shugaban kasar na yanzu Goodluck Jonathan da ya jagoranci dukkan ayyukan zaben shugaban kasar a wannan karo da kare ra'ayin demokradiyya. Daga nan sai ya yi kira ga dukkan jama'ar kasar Nijeriya da su amince da sakamakon zaben. A cewar mista Ban, idan akwai shakka, kamata ya yi a warware ta ta hanyar dokokin kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China