in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta kudu: Shugaban 'yan tawaye zai isa Juba a ranar 18 ga watan Afrilu domin kafa gwamnatin hadin kai
2016-04-08 10:31:42 cri
Shugaban 'yan tawayen Sudan ta Kudu Riek Machar ya bayyana cewa zai isa a ranar 18 ga watan Afrilu a birnin Juba, hedkwatar kasar, domin kafa wata gwamnatin rikon kwarya tare da shugaba Salva Kiir.

Mista Machar yayi wannan sanarwa a cikin wata wasikar da ya mika a ranar Laraba ga kwamitin hadin gwiwa na sanya ido da kimantawa (JMEC), wata hukumar dake kula ga sanya ido ga aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya a Sudan ta Kudu.

A cewar mista Machar, ya tabbatar da zuwasa birnin Juba a ranar 18 ga watan Afrilu, bayan wannan za a kafa gwamnatin wucin gadi tare da shugaba Kiir da kuma halatar taron ministocin kasa na wucin gadi. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China