in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya zartas da kuduri da sanarwar shugaba kan batun Sudan ta Kudu
2016-04-08 10:52:04 cri
Kwamitin sulhun MDD ya gudanar da wani taro a ranar 7 ga wata, wanda shugaban kwamitin sulhun na wannan wata kuma zaunannen wakilin Sin dake MDD Liu Jieyi ya shugabanta, inda aka zartas da kuduri mai lamba 2280 da sanarwar shugaba kwamitin kan batun Sudan ta Kudu.

A cikin kudurin, kwamitin sulhun ya tsaida tsawaita wa'adin rukunin masana na kwamitin sakawa Sudan ta Kudu takunkumi zuwa ranar 1 ga watan Yuli na shekarar 2016. Kana sanarwar shugaba ta yi maraba da bangarori daban daban na kasar Sudan ta Kudu da su aiwatar da yarjejeniyar warware rikicin kasar Sudan ta Kudu, ciki har da tabbatar da tsaro a Juba yadda ya kamata, kana sanarwar ta kalubalanci bangarorin da su ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar da nuna goyon baya ga jama'ar kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China