in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Chadi: An bude zaman taron kwamitin WHO na shiyyar Afrika karo na 65
2015-11-24 10:16:50 cri
Firaministan kasar Chadi, Kalzeube Payimi Deubet, ya jagoranci bikin bude zaman taro karo na 65 na kwamitin kungiyar kiwon lafiya ta duniya (WHO) dake shiyyar Afrika a ranar Litinin a birnin N'Djamena. Kwamitin shiyyar ya kasance wata babbar hukumar zartarwa ta kungiyar WHO a yankin Afrika, dake kunshe ministocin kiwon lafiya na kasashe mambobi 47.

A tsawon kwanaki biyar, mahalarta taron za su saurari da tattauna kan rahoton darektan game da ayyukan WHO a nahiyar Afrika tsakanin shekarar 2014 zuwa shekarar 2015, da kuma sauran batutuwan da suka jibanci kiwon lafiya, in ji Dokta Matshidisco Moeti, darektan WHO reshen Afrika.

Daga cikin batutuwan da za a tabo, akwai cigaban da aka samu kan ayyukan cimma burin muradun sabon karni na bunkasuwa dake nasaba da kiwon lafiya da tsarin cigaban kiwon lafiya na bayan shekarar 2015, da ma dabarun duniya kan gudanar da ayyukan kula da lafiyar jama'a, bincike kan kiwon lafiya da kokarin jama'a domin kiwon lafiya.

Mista Matshidisco Moeti ya kara da cewa, kwamitin shiyyar zai kuma tattauna game da asusun Afrika kan ayyukan gaggawa na kiwon lafiya ga jama'a, annobar cutar Ebola ta shekarar 2014, matsalar cutar shan inna da kuma tsare tsaren shiyyoyi wajen aiwatar da kasafin kudin tsarin WHO na shekarar 2016 zuwa shekarar 2017. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China