in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatan kamfani a Syria sun kubuta daga hannun IS
2016-04-08 10:56:57 cri
Bisa labarin da gidan talebijin na kasar Lebanon ya bayar a yau, an ce ma'aikata 140 daga cikin ma'aikata 344 na wani kamfanin harhada siminti na kasar Syria da dakarun kungiyar IS suka yi garkuwa da su a kwanakin baya sun cimma nasarar tsira.

Labarin ya bayyana cewa, kungiyar IS na ci gaba da yin garkuwa da sauran ma'aikatan kamfanin 204.

Kamfanin dillancin labarun Syria ya sanar da cewa, ba a iya yin mu'amala tare da ma'aikatan da aka yi garkuwa da su ba, yayin da bangarorin da abin ya shafa suna kokarin bincike don gano wurin da aka tsare su ciki.

Bisa labarin da gidan rediyon Sham FM na kasar Syria ya bayar a jiya, an ce, dakarun kungiyar IS sun kai hari ga wani kamfanin harhada siminti dake garin Dumayr dake dab da birnin Damascus na kasar a ranar 4 ga wannan wata, inda suka yi garkuwa da ma'aikatan kamfanin 344. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China