in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana ci gaba da kidaya kuri'u a kasar Uganda
2016-02-19 10:02:51 cri
A jiya Alhamis ne miliyoyin 'yan kasar Uganda suka fito kwansu da kwarkwata domin zaben sabon shugaban kasa da na 'yan majalisun dokokin kasar.

Rahotanni na cewa, tun da misalin karfe 7 na safe agogon wurin ne aka fara kada kuri'u a yawancin sassan kasar , koda ya ke an dan samu jinkiri fara kada kuri'a a Kampala,babban birnin kasar da kuma gundumomin da ke kewaye da shi.

Shugaban hukumar zaben kasar Badru Kiggundu ya ce, an samu jinkiri a wasu sassan birnin Kampala da yankunan da ke makwabtaka da shi ne sakamakon raba kayayyakin zaben a makare.Don haka ya yi kira ga 'yan kasar ta Uganda da su kwantar da hankulansu a lokutan zabe.

A nasa bangaren, babban mai sai do na kungiyar tarayyar Turai(EU) a zzabukan na Uganda Eduard Kukan, ya shaidawa manema labarai cewa, zaben ya gudana cikin lumana a sassan kasar daban-daban.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China