in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya sun ceto mutane fiye da 11000 daga hannun Boko Haram a wata guda
2016-04-07 10:01:41 cri
Rundunar sojin Najeriya ta ce kimanin mutane dubu 11 da 595 ne ta kwato, wanda mayakan Boko Haram suka yi garkuwa da su cikin wata guda kacal.

Kakakin rundunar sojin kasar Sani Usman ya tabbatar da cewar sojojin kasar sun ceto mutanen ne a lokacin wani simame a shiyyar arewa maso gabashin kasar tsakanin ranar 26 ga watan Fabrairu zuwa 31 ga watan Maris.

Ya ce yawancinsu, an same su ne a wasu kauyuka da garuruwa da mayakan Boko Haram suka boye su, sannan an karbo wasu daga hukumomin jamhuriya Kamaru.

Usman ya ce, dakarun kasar zasu ci gaba da gudanar da sintiri domin maido da zaman lafiya a shiyyar arewa maso gabashin kasar.

Hare haren Boko Haram ya yi sanadiyyar hallakar dubban jama'a, mafi yawa a shiyyar arewa maso gabashin kasar, tun bayan da suka kaddamar da yaki a shekarar 2009, a yunkurin kafa daular musulunci.

Sai dai dakarun Najeriya sun yi nasarar kwace mafi yawan yankunan dake karkashin ikon mayakan Boko Haram, amma har yanzu kungiya tana iya kaddamar da hare hare a wasu daga cikin yankunan kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China