in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A Najeriya an aikata laifuka sama da dubu 3 cikin watannin 10 ta yanar gizo
2016-03-31 11:47:38 cri
A jiya Laraba gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa, tsakanin watan Aprilun bara zuwa watan Fabrairu na bana an gano wasu laifuka kimanin dubu 3,599 da aka aikata ta hanyar yanar gizo, a ma'aikatu da hukumomin gwamnati a kasar.

Vincent Olatunji, shi ne mai rikon mukamin daraktan cibiyar bunkasa fasahar sadarwa na kasar NITDA, ya tabbatar da hakan a Abuja cewar, daga cikin adadin kimanin laifukan 2,500 ne aka yi nasarar aiwatar da su yayin da aka dakile saura.

Ya kara da cewar ana samun karuwar amfani da hanyoyin yanar gizo a kasar.

A cewarsa, sama da mutane miliyan 90 ne ke ta'ammali da yanar gizo a kasar a kullum, wajen harkokin kasuwanci na biliyoyin kudade.

Vincent, ya tabbatar da cewar, hukumar za ta ci gaba da iyakar kokarinta wajen bada kariya a fannin yanar gizo.(Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China