in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
NFF a Najeriya ta amince da gazawar Super Eagles
2016-03-31 10:40:27 cri
Babban jimi'i a hukumar kwallon kafa ta Najeriya Amaju Pinnick, ya fada a jiya Laraba cewar, kungiyar wasan kwllon kafan kasar Super Eagles, tayi dukkan iya bakin kokarinta don yin nasara a wasan share fage na shiga cin kofin Afrika AFCON na shekarar 2017.

Pinnick, ya fada a taron manema labarai a Abuja cewar, wanan abu tsautsayi ne, kasancewar kungiyar wasan ta yi iyakar kokarinta amma ba ta kai ga nasara ba.

Ya ce NFF zata mai da hankali, domin kungiyar ta samu shiga gasar share fagen na cin kofin duniya a 2018 wanda za'a buga wasan karshe a kasar Rasha.

NFF ta nuna farin ciki, kasancewar kungiyar Super Eagles na daga cikin wadanda ke da damar shiga gasar ta ta 2018.

Yanzu haka dai, kasar Masar ta samu nasarar shiga gasar ta 2017 a kasar Gabon, bayan da ta doke Najeriyar da ci 1 da nema.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China