in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta tsaurara tsaro a arewa maso gabashin kasar
2016-04-02 12:33:02 cri
Gwamnatin Najeriya ta tura karin jami'an tsaro kimanin dubu 5 domin gudanar da ayyukan tabbatar da tsaro a shiyyar arewa maso gabashin kasar.

Babban kwamandan rundunar tsaron jama'a na kasar Abdullahi Gana ya tabbatar da hakan, ya ce, hukumar ta dauki wannan mataki ne domin maye gurbin jami'an tsaron da suka rasu a yayin da suke bakin daga a yankunan kasar domin tabbatar da tsaro.

Ya kara da cewa, wannan shiri ya hada da tura jami'an 'yan sanda kimanin dubu 6 a yankunan shiyyar arewa maso gabashin kasar domin ci gaba da murkushe mayakan Boko Haram.

Ya ce wannan yunkuri da hukumar ta NSCDC ta yi, zai taimakawa kokarin da jami'an 'yan sandan kasar ke yi na wanzar da tsaro a yankunan kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China