Ta bayyana damuwarta bisa adadin da ke karuwa na masu kamuwa da cutar ta amai da gudawa, tare tabbatar da cewa wannan annoba ita ce mafi tsanani tun daga shekarar 1978. Gwamnatin kasar ta samu fadakar da jama'a kan matakan yaki da annobar, amma cigaba da aka samu ba mai gamsarwa ba ne, in ji madam Mwalimu a cikin wata sanarwa. Ruwan sama suna taimakawa sosai wajen bazuwar wannan cuta da ke da alaka da ruwa, ganin cewa ruwa mai tsafta da kuma kayayyakin kiwon lafiya sun kasance babu su sosai a cikin yawancin yankunan kasar. (Maman Ada)