in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ta yi kira ga jam'iyun kasar Burundi da su shiga cikin tattaunawa
2015-06-27 13:19:36 cri
Kwamitin sulhun MDD a ranar Jumma'an nan ta yi kira ga jam'iyun siyasa na kasar Burundi da ba tare da bata lokaci ba su shiga cikin tattaunawar da zai maida hankali a kan matakan da ya kamata a bi na kirkiro yanayi mai kyau da adalci a babban zaben kasar.

A cikin wata sanarwa Shugaba da aka amince da shi, mambobin kwamitin su 15 sun bayyana matukar damuwar su game da yanayin tsaro da siyasa a Burundin ganin matsowar babban zabe na Shugaban kasar da na majalissar dokoki.

Kwamitin tsaron ta yi taron gaggawa ne a kan Burundin a ranar Jumma'an nan da rana inda jakadan kasar ta Burundi a majalissar Albert Shingiro ya shaida mata cewa za'a gudanar da zaben kamar yadda aka rigaya aka shirya a ranar Litinin, duk kuwa da kiran da Babban magatakardar MDD Ban Ki-Moon ya yi a safiyar Jumma'a ga mahukuntar kasar na kara jinkirta zaben.

Rahotanni na nuna cewa jam'iyyun adawa za su kaurace ma zaben shugaban kasar Pierre Nkurunziza wanda yake neman komawa a karo na 3 abin da ya saba ma adadin na sau 2 da kundin tsarin mulkin kasar ta tanada. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China