in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Magatakardar MDD ya jinjina ma gudunmuwar 'yan Afrika dake sauran kasashen Duniya
2016-03-26 12:23:11 cri
Babban Magatakardar MDD Ban Ki-Moon a ranar jumma'an nan yayi jinjina ga 'yan Afrika dake zaune a sauran sassan duniya bisa ga gudunmuwar su ga al'umma da ya hada da bangarorin al'adu, magunguna, kimiyya da kuma imanin zukata, a lokacin da kasashen duniya suka taru domin martaba miliyoyin 'yan Afrika da aka tilasta su zama bayi.

A cikin sakon da ya aike domin ranar duniya na tunawa da wadanda suka fuskanci zamanin da kuma kasancewa cikin wadanda aka yi cinikin su a matsayin bayi, Mr Ban ya ce al'adu da gargajiya na musamman na 'yan Afrika zai cigaba da kyautata rayuwan kasashen da a baya suka kasasance cibiyoyin cinikin bayi.

A kowane shekara tun daga shekara ta 2007, MDD ta kebe ranar 25 ga watan Maris musamman domin tunawa da fiye da mutane , maza da mata da yara miliyan 15 da suka sha wahala suka kuma hallaka a lokacin fiye da shekaru 400 da aka yi na cinikin bayi, mafi girman hijiran mutane da aka taba samu a tarihi.

Ranar duniyar da aka kebe yana da zummar kara fadakar da al'umma ne game da hadarin da ke tattare da wariyar launin fata da kuma abin da zai haifar a yau.

Taken ranar a wannan shekarar shi ne " Tuna da bautan bayi : bikin abubuwan gado da al'adu na Afrika dake waje da kuma asalin su".(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China