in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kafofin yada labarai na duniya sun nuna babban yabo ga kasar Sin wajen zartas da dokar yaki da ta'addanci
2016-01-02 13:37:40 cri
A kwanan baya, zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ya zartas da dokar yaki da ta'addanci, wadda ta jawo hankulan gwamnatoci da masana da kafofin yada labarai na kasa da kasa. An bayyana cewa, ta'addanci da kungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi, manyan kalubaloli ne ga bil'adam. Zartas da dokar yaki da ta'addanci da Sin ta yi, wani muhimmin mataki ne mai amfani da aka dauka cikin lokaci wajen yaki da ta'addanci a duniya.

Wannan dokar da aka zartas da ita a ranar 27 ga watan Disamban bara, ta yi tanadi kan yadda za a tabbatar da kasancewar wata kungiya da membobinta a matsayi na ta'addanci, da yin rigakafi da aikin ta'addanci, da yadda za a gudanar da ayyukan leken asirrin da suka shafi ayyukan ta'addanci, da ma yadda za a gudanar da bincike da tinkarar harin ta'addanci, da yin hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa a wannan fanni da sauransu.

Tashar yanar gizo ta internet ta ma'aikatar harkokin waje ta Rasha ta ba da bayanin sharhi cewa, wannan ne muhimmin matakin da Sin ta dauka a fannin doka wajen yaki da kowane irin ta'addanci, wanda zai taimaka ga hadin gwiwa tsakanin Rasha da Sin a wannan fanni.

Ban da haka, a nasa bangare, wani masanin Kenya kan batun tsaro ya furta cewa, ta'addanci da masu tsattsauran ra'ayi, babban kalubale ne da bil'adam ke fuskanta, wadanda suka kawo babbar barazana ga zaman lafiya a duniya. Zartas da dokar yaki da ta'addanci da gwamnatin Sin ta yi, ya bayyana kwarin gwiwarta na yaki da ta'addanci.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China