in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan wasan kwallon kafar kasar Brazil sun yaba da ingancin kwallon kafa a Sin
2016-03-24 19:56:05 cri
'Yan wasan kwallon kafar kasar Brazil dake kwallo a nan kasar Sin, wato Renato Augusto da Gil, sun yaba da ci gaban da kwallon kafar kasar Sin ke samu a wannan lokaci, suna masu cewa nan gaba 'yan wasa masu yawa daga Brazil za su shigo fagen kwallon kafar kasar ta Sin.

Da yake bayyana kwarin gwiwar sa ga kwallon kafar kasar, Gil mai shekaru 28 da haihuwa, ya ce tun isowar sa kungiyar Shandong Luneng daga Corinthians a watan Janairu, ya sake samun gogewa da karsashi. Ya ce dukkanin wadanda suka san shi, sun san ba shi da wasa, kuma bai zo Sin a matsayin ritaya ba, ya zo ne domin ci gaba da kwazo na samun daukaka a sana'ar sa.

Augusto wanda shi ma ya baro Corinthians zuwa Beijing Guoan, cewa yayi ya zo ne domin baje basirar sa a fagen tamaula.

Tuni dai kocin kungiyar kasar Brazil Dunga, ya sanya 'yan wasan biyu cikin wadanda za su bugawa Brazil din wasannin share fagen cin kofin duniya tsakanin su da kasashen Uruguay da Paraguay.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China