in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Liberiya ta rufe kan iyakarta da Guinea sakamakon sake bullowar Ebola
2016-03-23 10:23:54 cri
Gwamantin Liberiya a ranar Talatan nan ta sanar da cewar ta rufe kan iyakarta da kasar Guinea bayan labarin mutuwar mutane biyu sakamakon cutar Ebola da ya sake bullowa a kasar.

Rundunar dakarun tsaron hadin gwiwwa na kasar Liberia ta rufe muhimman tasoshin bincike guda hudu dake kan iyakokin kasar a arewa maso gabashin gundumar Nimba tun ranar Jumma'an da ta gabata.

Sannan, an hana mazauna wurin da su yi ciniki tsakanin kasashen biyu.

Kasar Guinea dai a makon jiya ta tabbatar da cewar an samu sabbin mutane biyu wadanda suka kamu da cutar bayan da hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO ta sanar da karshen cutar a kasar yau fiye da watanni biyu da suka gabata. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China