in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNICEF ya bukaci a taimakawa yaran da Ebola ta halaka iyayensu
2016-01-15 09:50:57 cri
Asusun tallafawa kananan yara na MDD ko UNICEF a takaice ya bayyana cewa, kimanin kananan yara dubu 23,000 da suka rasa iyayensu sakamakon cutar Ebola ne suke bukatar goyon baya da tallafi.

Wannan kira na kunshe ne cikin wata sanarwa da MDD ta rabarwa manema labarai, bayan da aka sanar da kawo karshen cutar a kasar Liberia.

Sanarwar ta ce yanzu haka kasar ta Liberia tana karkashin shirin sa-ido na watanni uku, tun bayan da aka ayyana kawar da cutar a kasashen Guinea da Saliyon, a watanni Nuwamba da Disamban shekarar da ta gabata.

Asusun na UNICEF ya jaddada muhimmancin samarwa wadannan yara da suka shiga halin kunci a kasashe uku da cutar da ta fi addaba sutura, abinci, a kuma sanya su a makaranta.

Don haka, asusun na UNICEF ya yi kira ga al'ummomin kasashen Guinea, Liberia da Saliyo da su ci gaba da taimakawa wadannan yara, ta yadda za su farfado daga mummunan tasirin illar cutar ta Ebola.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China