in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun Najeriya sun hallaka mayakan Boko Haram 58
2016-03-23 09:40:34 cri
Rundunar tsaron Najeriya ta ce dakarun kasar sun yi nasarar hallaka mayakan Boko Haram 58 a wani musayar wuta na baya bayan nan tsakanin sojojin kasar da mayakan na Boko Haram.

Mai magana da yawun rundunar sojin Najeriyar Kanal Sani Usman ne ya tabbatar da hakan a jiya Talata.

Ya kara da cewar, sojojin sun yi nasarar gano wasu makaman gurneti biyu, da babura 52, da kuma buhunan kayan abinci a lokacin musayar wutar a jahar Borno dake shiyyar arewa maso gabashin kasar da maraicen ranar Litinin din da ta gabata, sai dai sanarwar ta ce soja guda ya rasa ransa a lokacin bata kashin.

Wannan sanarwa ta biyo bayan kashe 'ya'yan kungiyar ta Boko Haram 27 ne da dakarun Najeriyar suka yi a karshen makon jiya yayin wani artabu tsakanin sojojin da mayakan na Boko Haram.

Sakamakon irin wadannan galaba da dakarun kasar ke samu, gwamnatin Najeriya ta yi ikirarin karya lagon mayakan a yakin da kasar ke yi da ta'addanci. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China