in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya: Sojoji sun hallaka mayakan Boko Haram 27
2016-03-21 20:37:50 cri
Wata sanarwa da kakakin rundunar sojin Najeriya kanar Sani Kukasheka Usman ya fidda, ta ce a kalla mayakan Boko Haram 19 ne sojojin kasar suka hallaka, a sansanin 'yan kungiyar dake Dalore na jihar Borno.

Kanar Usman ya ce sojojin sun cimma wannan nasara ne yayin wani farmaki da suka kai maboyar 'yan kungiyar a jiya Lahadi, wanda hakan ya basu damar kubutar da wasu fararen hula 67, tuni kuma aka fara tantance wadanda suka samu kubutar, a sansanin 'yan gudun hijira na Dikwa.

Kaza lika sanarwar ta ce a ranar asabar ma, dakarun sojin sun hallaka wasu mayakan na Boko Haram su 7 a yankin Dawashi, yayin da suka yi musu kwantan bauna. Har wa yau a ranar ta asabar, wasu mayakan kungiyar 'yan kunar bakin wake sun gamu da ajalin su, sakamakon far musu da sojojin suka yi a kauyukan Kumala da Musafanari.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China