in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da makon hana wariyar launin fata a Afrika ta kudu
2016-03-15 11:13:52 cri
Kungiyoyi masu zaman kansu a ranar Litinin din nan suka kaddamar da makon hana wariyar launin fata, irin shin a farko a kasar, a wani kokari da ake yin a rage zaman dar dar da ake yi game da hakan.

Gangamin na da nufin karfafa tattaunawa a bainal jama'a a kan batutuwan da suka shafi wariyar launin fata ta inda za'a aiwatar da shirye shirye da dama, in ji wadanda suka shirya bukin.

Gidauniyoyin Nelson Mandela da Ahmed Kathrada su ne suka shirya gangami cikin hadin gwiwwa da a kalla sauran kungiyoyi 80 karkashin shirin hana wariyar launin fata a Afrika ta kudu.

Wadanda suka shirya gangamin sun bukaci al'ummar kasar ta Afrika ta kudu da su gano, fadakar tare da aiwatar da shiri mai kyau da dabaru da zai hana wariyar launin fata da rage tare da magance wariyar launin fata baki daya, a kuma fatan al'ummomin kasar su yi cudanya su kuma dauki mataki na kalubalantar duk wani nau'in wariyar launin fata a kuma gyara shi inda ya auku. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China