in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya za ta janye wasu sojojinta daga cikin rundunar kiyaye zaman lafiya na MDD a Mali
2013-08-02 10:54:05 cri
Kakakin MDD Martins Nesirky ya sanar a wajen taron manema labarai da aka saba yi kullum cewa majalisar ta samu sanarwa a hukumance daga kasar Nijeriya cewa za ta janye wasu dakarunta daga cikin rundunar sojin kiyaye zaman lafiya a kasar Mali.

Nesirky yayi bayanin cewa an sanar ofishin kiyaye zaman lafiya na majalisar cewa Nijeriya zata janye wasu dakarunta na soji,yana mai bayanin cewa sai dai hakan ba ya nufin gaba daya ba,domin za ta bar wasu da suka hada da sojoji ma'aikatan kiwon lafiya da 'yan sanda.

Kakakin a don haka ya isar da sakon godiya ga kasar Nijeriya bisa ga taimakon da ta rika bayarwa kawo yanzu ga ayyukan kiyaye zaman lafiya na majalisar.

Ya kara da cewa ofishin kula da ayyukan kiyaye zaman lafiya na cigaba da tuntubar sauran kasashe don su bada gudumuwar rundunar su ga ayyukanta a kasar Mali.

A watan Fabrairu ne Nijeriya ta aika da sojoji 1,200 zuwa ga rundunar kasashen Afrika ta tallafawa Mali AFISMA a matsayin gudummuwarta ga ayyukan kiyaye zaman lafiya a kasar Mali. A watan Afrilu kuma kwamitin tsaro na MDD ta amince da rundunar kiyaye zaman lafiya na majalisar MINUSMA mai sojoji fiye da 12,600 da ta karbi ragamar jagoranci daga hannun AFISMA,abin da yasa a ranar 1 ga watan Yuli aka kammala ayyukan musayar jagoranci tsakanin rundunar guda biyu a Bamako babban birnin kasar Mali.Yanzu haka MINUSMA ce rundunar mafi girma ta uku na majalisar a duniya.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China