Wata sanarwar da kakakin fadar gwamnatin Femi Adesina ya fitar, ta bayyana cewa, shugaba Buhari zai gana da shugaba Obiang Nguema Mbasogo a Guinea, game da hanyoyin da kasashen biyu za su bi wajen ba da kariya ga al'ummunsu, da yankunan Niger Delta a Najeriya, da kuma na zirin tekun Guinea.
Kaza lika a gobe Talata ake sa ran sassan biyu, za su rattaba hannu kan wasu yarjeniyoyin hadin gwiwa na kariya ga tekun kasashen nasu, ta yadda za a kai ga inganta sintiri da wanzar da doka da oda a kan teku. Adesina ya kara da cewa, shugaba Buhari da Mr. Mbasogo za su zanta game da hanyoyin dakile laifuka, kamar na fashin teku, da satar mai, da barnata kayayyakin hakar mai, fasa kwaurin makamai da safarar bil'adama a yankin tekun Guinea.
Har ila yau bangarorin biyu za su nazarci batun sauya lokacin tarukan hadin gwiwa na kungiyar ECOWAS da takwarar ta kasashen dake tsakiyar nahiyar Afirka, game da ci gaban dangantakar kungiyoyin a fannin yaki da ta'addanci da tsattsauran ra'ayi, a yammaci da tsakiyar Afirka. (Saminu Alhassan)