in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi maraba da sakamakon karshe na babban zaben kasar CAR cikin lumana
2016-03-05 10:06:51 cri
MDD ta yi maraba da sakamakon da aka samu cikin lumana na babban zaben kasar Jamhuriyar Afrika ta tsakiya, wanda Faustin-Archange Touadera ya samu nasara, in ji kakakin majalissar a ranar Jumma'an nan.

Zaben wanda ya gudana cikin lumana da samun fitowar 'yan kasar soai suka kada kuri'ansu, in ji Frahan Haqq, mataimakin kakakin majalissar a ganawarsa da manema labarai, yana mai misali da sanarwar hadin gwiwwa ga manema labarai da majalissar ta yi tare da kungiyar AU, da kungiyar tarayyar tattalin arzikin kasashen tsakiyar Afrika ECCAS, kungiyar tarayyar kasashen Tuari EU da kungiyar kasashen renon Faransa La Francophonie a ranar Jumm'a.

Hukumomin gaba dayan su sun mika sakon taya murnan su ga zababben shugaban kasar Faustin-Archange Touadera, inda suka bayyana goyon bayan su bisa ga kudurin shi na inganta tattaunawa da sulhu a cikin kasar, in ji Farhan Haq.

Hukumomin kasashen duniyan za su ci gaba da ba da goyon bayansu ga sabon kokarin da kasar Jamhuriyar Afrika ta tsakiya ke yi yadda ya kamata, in ji shi. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China