in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Faustin-Archange Touadera ya lashe zaben CAR
2016-02-21 13:23:52 cri
Tsohon firaministan Jamhuriyar Afirka ta tsakiya Faustin-Archange Touadera ya lashe zaben shugabancin kasar na ranar 14 ga watan Fabrairu.

Hukumar zaben kasar wanda ta bayyana haka a jiya Asabar ta ce Touadera ya samu kashi 62.71 cikin 100 na kuri'un da aka kada.

Touadera dan shekaru 58 ya taba zama mataimakin shugaban jami'ar Bangui, kana ya yi aiki a matsayin firaministan kasar a zamanin Francois Bozize daga shekarar 2008 zuwa 2013.

A wani labarin kuma, abokin takararsa a zaben shugabancin kasar Anicet-Georges Dologuele ya ce, zai mutunta sakamakon wucin gadin da hukumar zaben kasar ta sanar. Dologuele ya ce, ya yi hakan ne domin tabbatar da zaman lafiya a kasar.

Sakamakon wucin gadin da hukumar zaben kasar ta fitar yana nuna cewa, tsohon firaminista Dologuele ya samu kashi 37.29 cikin 100 na kuri'un da aka kada a zaben na ranar 14 ga watan Fabarairu.

Jamhuriyar Afirka ta tsakiya dai tana kokarin bude wani sabon babi ne, bayan shafe shekaru 3 tana fuskantar tashin hankali tun lokacin da tsohon shugaban 'yan tawayen Seleka Micheal Djotodia ya hambarar da Francois Bozize daga karagar mulkin kasar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China