in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala aikin yaki da talauci na kasar Sin na shekarar 2015
2016-03-01 10:32:58 cri

Mai magana da yawun ofishin yaki da talauci na majalisar gudanarwar kasar Sin, kuma shugabar hukumar tsara manufofi da dokoki ta kasar Su Guoxia, ta bayyana a ranar Asabar din da ta gabata cewa, bisa alkaluman da hukumar kididdiga ta kasar Sin ta gabatar, yawan matalauta a kauyukan kasar Sin ya ragu, daga miliyan 70 da dubu 170 a shekarar 2014, zuwa miliyan 55 da dubu 750 a shekarar bara, wanda hakan ke nuna cewa an kammala aikin yaki da talauci na shekarar 2015, wato na rage yawan mutane masu talauci da fiye da mutum miliyan 10.

Su Guoxia ta kara da cewa, yawan matalauta a kasar Sin a shekarar 2015 ya ragu da miliyan 14 da dubu 420 bisa na shekarar 2014, kana yawan mutane da mai yiwuwa za su kasance cikin kangin talauci a kasar ya ragu daga kashi 7.2 cikin dari zuwa kashi 5.7 cikin dari. Kaza lika saurin ayyukan yaki da talauci ya karu bisa na shekarar 2014.

Hukumomi daban daban da abin ya shafa sun gabatar da matakan taimakawa yankuna masu fama da talauci. Kana bangarori daban daban sun tattara kudi da yawansa ya kai yuan biliyan 10 don yaki da talauci, kudaden da yawansu ya karu da ninka biyu bisa na shekarar 2014.

A shekarar 2015, an kara samar da kudi na musamman don yaki da talauci, ciki har da kudin da gwamnatocin lardunan kasar suka samar wato Yuan biliyan 33.5, wanda ya karu da kashi 25 cikin dari bisa na shekarar 2014. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China