in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
2016: Sin na da burin fidda mazauna karkara miliyan 10 daga kangin talauci
2015-12-25 09:30:13 cri
Darakta mai lura da ofishin yaki da talauci da samar da ci gaba, a kwamitin tsakiyar Jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin Liu Yongfu, ya ce a shekarar 2016 dake tafe, za a aiwatar da manufofi da dama, wadanda za su ba da damar fidda mazauna yankunan karkara a kalla miliyan 10 daga kangin talauci.

Mr. Liu wanda ya bayyana hakan a jiya Alhamis, ya ce sassa daban daban za su yi hadin gwiwa don tabbatar da nasarar wannan kuduri. A cewar sa hakan bangare ne na aiwatar da manufofin ci gaban kasar Sin, tsakanin shekarar 2014 zuwa 2020, wanda ya tanaji fidda a kalla mutane miliyan 10 daga kangin fatara a duk shekara.

Liu ya yi hasashen cimma nasarar da aka sanya gaba a bana, duba da yadda aka samar da isassun kudaden taimakawa masu karamin karfi a fadin kasar.

Jami'in ya kara da cewa, tuni Sin ta cimma nasarar fidda al'ummun ta mazauna karkara kusan miliyan 100 daga halin matsi, daga shekarar 2010 ya zuwa yanzu, yayin da kuma ake ci gaba da kokarin tallafawa karin wasu mutanen miliyan 60 nan da karshen shekarar 2020. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China