in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojan tsaro na Iraki ta sanar da kwace cibiyar birnin Ramadi daga hannun kungiyar IS
2015-12-28 14:13:18 cri
Da daren jiya Lahadi ne rundunar sojan kasar Iraki, ta sanar da kwace cibiyar birnin Ramadi, fadar mulkin jihar al-Anbar dake yammacin kasar daga hannun kungiyar IS bayan kwashe kwanaki ana dauki ba dadi tsakanin sassan biyu.

Birnin Ramadi dai shi ne babban birnin jihar al-Anbar, jiha mafi girma a kasar ta Iraki. Tun kuma cikin watan Mayu na wannan shekara ne kungiyar IS ta mamaye shi, inda mayakan ta suka maida shi muhimmin sansanin su a yammacin kasar.

Rundunar sojin kasar ta fayyace cewa, tun da fari ta kwace wani matsugunin kungiyar dake cibiyar birnin Ramadin, kafin daga bisani ta mamaye babban ginin gwamnatin jihar dake wurin.

Birnin Ramadi na da muhimmin matsayi, kuma kwace shi daga hannun mayakan na IS zai taimakawa sojojin gwamnatin mamaye biranen Fallujah, da Mosul daga ikon kungiyar ta IS.

Rahotanni sun nuna cewa, fadin yankunan kasar da kungiyar IS ke mamaye da su na ci gaba da raguwa. Kaza lika jaridar harkokin tsaro ta Jane's Defence Weekly ta kasar Birtaniya, ta fidda wani rahoto dake cewa, a shekarar 2015 din nan, fadin yankunan da kungiyar ta mallaka a kan iyakar kasashen Iraki da Sham, ya ragu da kashi 14 cikin dari.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China