in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Barcelona zai kafa kwalejin wasan kwallon kafa a Najeriya
2016-02-24 16:02:28 cri

Gwamna Akinwunmi Ambode na jahar Legas dake tarayyar Najeriya, ya bayyana cewar kulub din wasan kwallon kafa na Barcelona dake kasar Sifaniya, ya kammala shiryawa tsaf domin kafa kwalejin horas da 'yan wasan kwallon kafa a Afrika wadda kulaf din zai gina a jahar Legas.

Ambode ya bayyana hakan ne a yayin da ya karbi bakuncin manyan jami'an kulob din, wanda ya zama na gaba-gaba a duniya ta fuskar fasahar wasan kwallon kafa.

Gwamnan ya bayyana wannan al'amari a matsayin wani babban abin tarihi a jihar, sannan ya bayyana cewar abin farin ciki ne, kasancewar lamarin ya zo dai dai lokacin da gwamnatin ke shiye shiryen karbar bakuncin wasannin gudun famfalaki wato marathon na kasa da kasa.

Ambode ya bayyana muhimmancin wasanni wajen samar da ci gaba, ya kara da cewer, harkar wasanni tana taimakawa musamman wajen samar da ayyukan yi ga matasan jahar ta Legas.

Pau Vilanovai Vila-Abadal, shi ne daraktan harkokin kasuwanci, na kungiyar wasannin kwallon kafa ta Barcelona, ya kuma bayyana cewa Barcelona ta yanke shawarar kafa kwalejin ne a Legas, saboda yawan al'umma da jihar ke da shi, da kuma samar da damammaki ga jihar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China