in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Algeria da Tunisiya na goyon bayan warware rikicin siyasar kasar Libya
2016-02-15 10:03:47 cri
Kasashen Algeria da Tunisiya sun jaddada goyon bayansu wajen warware rikicin siyasar kasar Libya, sannan sun yi fatali da yunkurin amfani da karfin soji wajen warware rikicin kasar dake shiyyar arewacin Afrika wacce ke fama da rikici.

Ministan harkokin wajen Tunis Khemaies Jhinaoui ya shedawa 'yan jaridu bayan wata ganawa da takwaransa na kasar Algeriya Ramtane Lamamra , inda ya bukaci bangarorin da basa ga maciji da juna a Libyan dasu zauna a teburin sulhu da bangaren gwamnatin kasar domin warware takaddamar dake tsakaninsu don kafa gwamnatin hadin kan kasa.

Bugu da kari, babban jami'in diplomasiyya na kasar Algeriyar ya bayyana cewar, kasarsa ta yi amanna cewar amfani da karfin soji ba zai taba yin tasiri ba wajen kawo karshen rikicin kasar ta Libya.

Ya ce suna fatar kasancewa makwabta masu taka muhimmiyar rawa wajen warware rikicin kasar Libya amma ba masu haddasa matsala ba.

Ya kara da cewar, a kwanan nan wasu kasashen yammacin duniya sun sha yunkurin amfani da karfin tuwo wajen fatattakar mayakan kungiya mai fafutukar kafa daular musulunci wato IS daga kasar.

Kasar Libya ta tsunduma cikin rudani ne tun bayan kifar da gwamnatin tsohon shugaban kasar Muammar Gaddafi a shekarar 2011.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China