in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar gudanarwar kasar Libya ya fidda sabbin sunayen ministocin kasar
2016-02-15 13:29:43 cri
Majalisar gudanarwar kasar Libya ya fitar da sunayen sabbin ministocin gwamnatin hadin gwiwa da ta kunshi kabilu daban daban na kasar, a wani taro da aka yi a yankin karkara Skhirat na birnin Rabat hedkwatar kasar Morocco.

Gwamanatin hadin gwiwar da ake shirin kafawa za ta kunshi mambobi 18, ciki har da ministoci 13 da kananan ministoci 5, a cikin wadannan mutane, akwai Mata 3. Sa'an nan bangarorin daban daban na kasar na da wakilai cikin gwmantin.

A ranar 19 ga watan da ya gabata, majalisar gudanarwar firaministan kasar ya fidda sunayen ministocin gwamnatin hadin gwiwa, kuma bisa wannan takarda, an ce, gwamnatin tana kunshe da mambobi 32,amma ba a zartas da wannan kuduri cikin majalisar dokokin kasar ba.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China