in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana da Iran sun sha alwashin yakar ta'addanci
2016-02-16 10:44:10 cri
Shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama da takwaransa na kasar Iran Hassan Rouhani, sun amince da hada gwiwa domin yakar ayyukan masu tsattsauran ra'ayi.

A wata sanarwar da aka fitar a Litinin din data gabata, shugabannin biyu sun cimma matsayar ne bayan tattaunawar sirrin da suka gudanar a matsayin wani bangare na ziyayar aiki ta kwanaki biyu da shugaba Mahama ya kai a jamhuriyar musuluci ta Iran.

Da yake zantawa da 'yan jaridu bayan kammala ganawar tasu, shugaba John Mahama, ya bayyana cewar ya zama tilas su hada gwiwa a yayin da ake fuskantar yawaitar ayyukan masu tsattsauran ra'ayi a duniya.

Ya kara da cewar, matsalar hare hare daga masu tsattsauran ra'ayi da 'yan ta'adda babbar barazana ce ga duniya baki daya, kuma za'a yi nasarar magance ta ne kadai ta hanyar hadin gwiwa tsakanin kasashe.

Mahama ya ce, matsalar masu tsattsauran ra'ayi ta shafi kasashen Afrika, misali: yanayin da ake ciki a Libya yana shafar yankunan kasashen Sahel na Afrika, ga rikicin mayakan Al-Qaeda a yankin Maghreb, da kuma na Boko Haram, dukkanin wadannan matsaloli ne dake barazana ga zaman lafiyar Afrika.

Shugaban na Ghana, ya bayyana cewar, sun tattauna muhimman batutuwa biyu da suka hada da yakar akidojin masu tsattsauran ra'ayi ta hanyar al'adu, sannnan sai amfani da dabaru irin na zamani ta hanyar hadin gwiwa don yakar ta'addanci.

Ban da haka kuma, Mahama ya yabawa Rouhani game da irin matakan da yake dauka domin yakar ta'addanci.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China